Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ranar Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi ta Duniya: Ƙungiyoyi Sun Yi Gangamin Wayar da Kai, Sun Nemi Haɗin Kan Al’umma Don Daƙile Shaye-shaye a Kano
Kano

Ranar Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi ta Duniya: Ƙungiyoyi Sun Yi Gangamin Wayar da Kai, Sun Nemi Haɗin Kan Al’umma Don Daƙile Shaye-shaye a Kano

June 26, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260626 WA0013

Ƙungiyoyin farar hula masu yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano sun yi kira ga gwamnati, iyaye, malamai da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai domin daƙile matsalar shaye-shaye, wadda suka bayyana a matsayin babbar barazana ga makomar matasa da ci gaban al’umma.

An bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin gangamin wayar da kai na “My Voice Against Drugs Walk”, da aka shirya domin bikin Ranar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Duniya, ranar da Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) ta ware a duk shekara domin wayar da kan al’umma kan illolin shaye-shaye da fataucin miyagun ƙwayoyi.

Gangamin ya samu halartar Foundation for a Drug-Free World, Coalition of NGOs Kano, da sauran ƙungiyoyin sa-kai, inda mahalarta suka yi tattaki tare da isar da saƙonnin da ke ƙarfafa matasa su guji shaye-shaye.
Da take jawabi, Maryam Muhammad, daga ƙungiyar da ke yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano, ta ce shaye-shaye na ci gaba da lalata rayuwar dubban matasa tare da haddasa matsalolin tsaro, zaman lafiya da tattalin arziki.

Ta ce lokaci ya yi da kowa zai ɗauki nauyin da ya rataya a wuyansa wajen kare matasa daga fadawa cikin shaye-shaye da kuma hana masu safarar miyagun ƙwayoyi samun damar yaudararsu.

“Ba gwamnati kaɗai za ta iya magance wannan matsala ba. Iyaye, malamai, shugabannin addini, ƙungiyoyin al’umma da matasa kansu dole ne su haɗa kai domin kare al’umma daga wannan annoba,” in ji Maryam Muhammad.

A nata jawabin, Ladidi Adamu Abdullahi ta bayyana cewa wayar da kai na daga cikin manyan hanyoyin rage yawaitar shaye-shaye, tana mai kira ga ƙungiyoyi da cibiyoyin ilimi su ci gaba da gudanar da shirye-shiryen ilmantar da matasa kan haɗarin miyagun ƙwayoyi.
Hakazalika, Aisha Haruna Kabuga, daga Ƙungiyar Kare Haƙƙin Yara, ta ce yara da matasa ne suka fi fuskantar haɗarin fadawa cikin tarkon masu safarar miyagun ƙwayoyi, saboda haka ya zama wajibi iyaye su ƙara sa ido kan tarbiyyar ‘ya’yansu.

Ita ma Maryam Hassan ta buƙaci hukumomin gwamnati da masu ruwa da tsaki su ƙara tallafa wa shirye-shiryen wayar da kai da kuma samar da cibiyoyin gyaran hali domin taimaka wa waɗanda suka kamu da shaye-shaye su dawo cikin al’umma.

Mahalarta gangamin sun jaddada cewa nasarar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ba za ta samu ba sai an haɗa hannu tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro, ƙungiyoyin farar hula da daukacin al’umma.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

YAƘI DA SHA DA FATAUCIN MIYAGUN ƘWAYOYI A KANO: Babban Kalubale Ne Ke Gaban Kwamitin Muhuyi Rimingado

June 26, 2026

Kano: Fitaccen Ɗan Kasuwar Man Fetur, Audu Manager, Ya Rasu Yana Da Shekaru 68

June 4, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Kano: Fitaccen Ɗan Kasuwar Man Fetur, Audu Manager, Ya Rasu Yana Da Shekaru 68

June 4, 20266
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.