Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ƙasashen da Trump ya nemi su aika jiragen yaƙi Hormuz sun yi watsi da buƙatar
Babban Labari

Ƙasashen da Trump ya nemi su aika jiragen yaƙi Hormuz sun yi watsi da buƙatar

March 16, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
709995 750x375

Har yanzu babu ƙasa ko guda 1 da ta amsa buƙatar Donald Trump wajen aika jirgi mashigin Hormuz cikin ƙasashe 5 da shugaban na Amurka ya nemi su aike da jiragen yaƙinsu na ruwa tare da sojojinsu don yiwa jiragen dakon mai rakiya a mashigin na Hormuz da Iran ta kulle.

A jiya Asabar ne Trump ya nemi ƙasashen China da Faransa da Japan da Korea ta kudu da kuma Birtaniya kan su aike da jiragen yaƙi zuwa mashigin na Hormuz don ƙalubalantar shingen da Iran ta sanya wanda ya hana safarar makamashi.

Gwamnatin Najeriya ta ɓullo da shirin samar da tsayyayiyar wutar sola a asibitoci 371

Japan ce ƙasa ta farko da ta fara mayar da martani kan kiran na Trump inda ta ce babu yadda za a yi su tashi jirgin yaƙi zuwa mashigin na Hormuz kawai don Trump ya buƙaci haka.

A gefe guda Birtaniya ta bakin ministan tsaron ta ya shaidawa wata kafar labarai ta Amurka cewa, ƙasar yanzu haka na tattaunawa da ƙawayenta don laluben hanyoyin da za a dawo da hada-hadar makamashi a yankin na gabas ta tsakiya.

China wadda ke matsayin ƙawa ga Iran ta nanata cewa za ta so ɓangarorin da ke yaƙar juna su kawo ƙarshen shigar da ƴan baruwanmu cikin rikicin yayinda ta yi fatan dawowar hada-hadar makamashi don amfanin jama’a.

Faransa cikin wani saƙo da ministan harkokin wajen ƙasar ya wallafa a shafin X ya ce ƙasar ba zata aika da jiragen yaƙi mashigin na Hormuz ba, haka zalika babu wani jirgin yaƙin Faransa na ruwa ko na sama da za a ga gilmawarsa ko kuma zuwansu gabashin tekun na Mediterranean.

Sai dai an jiyo shugaban Korea ta kudu na cewa suna nazartar buƙatar ta Trump kuma suna tattaunawa da Amurka kan batun.

Kafin yanzu dai wata sanarwar ma’aikatar tsaro da ta kasuwanci a Amurkan sun bayyana cewa ƙasar ba zata yi kasadar tura dakarun Sojin ruwa kawai don baiwa jiragen dakon makamashi kariya a mashigin na Hormuz ba.

Akwai fargabar cewa Iran ta dasa ababen fashewa a mashigin na Hormuz.

 

RFI

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.