Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Najeriya ta ɓullo da shirin samar da tsayyayiyar wutar sola a asibitoci 371
Afrika

Gwamnatin Najeriya ta ɓullo da shirin samar da tsayyayiyar wutar sola a asibitoci 371

March 14, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1773460183395

Gwamnatin tarayya tare da guiwa da Gavi da ke samar da magunguna da asusun kula da ƙananan yara (UNICEF), za ta sanya wutar sola a asibitocin a matakin farko (PHCs) guda 371 a jihohi 16 ciki har da babban birnin tarayya Abuja domin inganta allurar rigakafi da kula da marasa lafiya musamman a yankunan da aka bi buƙatar tallafin.

An ƙaddamar da fara shirin saka wutar ne a wani biki da hukumar bunƙasa asibitoci a matakin farko (NPHCDA) ta shirya a Abuja a ranar Alhamis.

Kano, Sokoto da jihohi tara na iya fuskantar ɓarkewar cutar sankarƙau – NiMet

A yayin da yake magana, babban daraktan NPHCDA, Muyi Aina, ya ce, saka wutar solar zai samar da tsayayyiyar wutar lantarki ga asibitocin da ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Mista Aina ya ce tsayayyiyar wutar lantarki na da muhimmancin gaske wajen kula da alurarorin rigakafi da gudanar da ayyukan da za su ceci rayuka kamar allurar rigakafi, da lafiyar mata masu juna biyu da masu neman agajin gaggawa.

Ya ce, wutar lantarki ba abu ne na jin daɗi ba, abu ne da ya zama wajibi wajen gudanar da ayyuka da taimaka wajen hauhuwar yara cikin kwanciyar hankali da daddare.

Inganta asibitoci PHCs:

Mista Aina ya ce, shirin sa wutar solar wani ɓangare ne na ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a asibitoci a matakin farko da ba wa mutane damar samun kulawar lafiya.

Ya kuma ce, baya ga wutar salar, gwamnati ta ƙaddamar da shirin farfaɗo da asibitoci a matakin farko a yayin da ake kan gyaran asibitoci 4,000.

Mafi yawan aibitocin da aka yi wa gyara an sa musu wutar sola a yayin da aje ci gaba da sa wutar solar a sauran asibitocin.

Shirin farfaɗo da asibitoci ha haɗa har da samar da kayayyakin more rayuwa kamar wutar lantarki da ruwa da abubuwan tsabtace asibiti tare da magungunan da ake da buƙata domin gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Allurar rigakafin:

Haka kuma, a yayin da take magana, babbar jami’in Gavi, Sania Nishtar, ta ce, kamfanin na su ya zuba hannun jarin sama da Dala biliyan 2.4 a shirin allurar rigakafin Najeriya a tsawon shekaru biyu da suka gabata.

Ms Nishtar, wadda ta wakilci babban manajar Gavi, Edna Harimenshi, ta ce, wannan haɗin guiwa ya ba da gudunmowa wajen inganta yadda aike allurar rigakafi wanda ya karu daga kaso 27% a 2001 zuwa kaso 67% a 2024.

A cewarta, ci gaban ya sa Najeriya ta cike giɓin allurar rigakafi da kai wa ga yaran da ba su samu allurar rigakafi ba.

Ta kuma ce ci gaban ya ta’allaƙa ne da tsayayyiyar wutar lantarki.

“Ƙaddamar da shirin wani mataki ne na magance ƙalubalen da aka daɗe ana fama da su.”

Haka kuma wakilin UNICEF a Najeriya, Wafaa Saeed Abdelatef, ya yaba wa ƙoƙarin da Najeriya ke yi wajen ƙarfafa asibitoci a matakin farko da faɗaɗa allurar rigakafi.

Ms Abdelatef ta ce wannan shiri a shekarun baya, ya tallafa wa yara waɗanda ba su samu allurar rigakafi ba tare da bayyana da shirin da muhimmin abu da zai rage bambancin da ake samu wajen neman lafiya.

Ta ce tsayyayiyar wutar lantarki a fannin lafiya mihimmin abu ne ga ayyukan allurar rigakafi da lafiyar mata masu juna biyu da sauran ayyukan tallafa wa al’umma.

Ita ma a jawabi, sakatariyar lafiya da muhalli ta birnin tarayya Abuja, Adedolapo Fasawe, ta ce, shirin muhimmi ne wajen inganta asibitoci a matakin farko ga mutane masu rauni,

Ms Fasawe ta ce samar da tsayayyiyar wuta na da muhimmanci wajen kula da allurar rigakafi wadda ke buƙatar wuri mai sauyi da ba da magani da tabbatar da yanayi mai kyau ga mata masu juna biyu a lokacin haihuwa.

Game da shirin Gavi-CDS3:

Shirin Gavi-CDS3, shiri ne da ya ƙunshi masu ruwa da tsaki daban-daban a gida da ƙasashen waje. Cibiyar eHealth Systems Africa ta sa ka wutar lantarki a asibitoci a matakin farko 238 a yayin da kamfanin Differ Community Power ya sa ka wutar lantarki a asibitoci 133 a faɗin Arewa maso gabas.

UNICEF ce ta kula da aikin tare da NPHCDA da hukumar bunƙasa asibitoci a matakin farko da taimakon ƙungiyar ƙasashe rainon Ingila da.

Jihohin da suka ci gajiyar shirin ciki har da Abuja, sun sha alwashin kula da kayayyakin domin tabbatar da ci gaban ayyukansu.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.