Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin jihar Kano tayi fatali da sabbin Dokokin Haraji a Najeriya
Afrika

Gwamnatin jihar Kano tayi fatali da sabbin Dokokin Haraji a Najeriya

January 2, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin Jihar Kano dake arewacin Najeriya, ta bayyana matsayarta kan sabbin dokokin haraji da ake tattaunawa a Majalisar dokokin kasar.

Mataimakin gwamnan jihar Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya wakilci Gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne lokacin bikin sabuwar shekarar 2025 da aka gudanar a Filin Mahaha da ke Ƙofar Naisa.

Wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na mataimakin gwamnan Ibrahim Garba Shu’aibu ya fitar, Gwarzo, ya ce “Waɗannan dokokin haraji ba su ne mafita ga matsalolin tattalin arziƙinmu ba”.

Ya ƙara da cewa jihar Kano ba zata yarda da kowace doka da za ta cutar da walwalar al’ummarta ba.

Haka kuma Kwamared Aminu ya yaba wa jajircewar al’ummar Kano wajen fuskantar ƙalubalen tattalin arziƙi, inda ya ce sam harajin bai dace ba.

Ya ƙara da cewa kamata ya yi gwamnati ta fi mayar da hankali kan yaƙi da talauci da yunwa, musamman a yankin Arewa, wanda ke fama da tsadar rayuwa da rashin tsaro.

Mataimakin Gwamnan, ya na mai jaddada nasarorin gwamnatin Kano a ɓangarorin lafiya, ilimi, samar da hanyoyi, da tallafin karatu zuwa ƙasashen waje.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta umarci masu gudanar da sana’ar gwangwan da su dakatar da sayo kayayyakin daga yankin Arewa maso Gabas

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Karya dokar Tuki ke Jawo Asarar Dukiya da Rayuka Sakamakon Haifar da Hatsari

June 18, 2025

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya dawo gida Najeriya Bayan gudanar da Ibadar aikin Hajji 2025.

June 18, 2025

Gwamnatin jihar kano tayi kira ga iyaye da su dinga sanya idanu akan ƴaƴan su mata wajen sauke duk wani nauyi da yake kan su

May 28, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.