Shugaban hukumar zaɓen Najeriya Farfesa Joash Amupitan ya gargaɗin gidajen yaɗa labarai kan yaɗa labaran bogi, yana gargaɗin cewa sahihancin zaɓen 2027 na wuyan yadda kafafen yaɗa labaran Najeriya suke bayyana abubuwan da ke faruwa.
Shugaban ya bayyana haka ne a yayin taron kafafen yaɗa labarai Najeriya karo na 81 da ya gudana a yau Laraba, inda ya nanata cewa fagen yaɗa labarai ya zama wani sabon dandalin yaƙin neman zabe na zamani.
Gwamnatin Kano ta musanta hannu a yarjejeniyar fili a makarantar FGC
Yana cewa babu wata barazana kan gudanar da sahihin saɓe, sai dai yadda kafafen yaɗa labarai marasa sahihanci kan haifar da barazanar hakan ta hanyar yaɗa labaran ƙanzon gurege.
Farfesa Amupitan ya nanata buƙatar bin dokar aikin watsa labaran siyasar ta 2026, wadda idan aka bi ta za a samu saukin abubuwan da ke faruwa.
