An nada dan marigayi Ayatullah Ali Khamenei a wannan mukami ne yayin da ake dab da cika kwanaki 10 da barkewar yaki a tsakanin Iran da Amurka da Isra‘ila wanda ya tsayar da harkoki a yankin Gabas ta Tsakiya.
Majalisar manyan malaman Iran ce ta sanar da cewa Mojtaba Khamenei ne zai gaji mahaifinsa a matsayin babban jagoran ƙasar.
An sanar da naɗin Mojtaba Khamenei mai shekara 56 a ranar Lahadi, bayan ƙuri’ar da majalisar malaman addini ta ƙasar ta kaɗa domin zaɓar wanda zai gaji mahaifinsa.
An haifi Mojtaba Khamenei a ranar 8 ga watan Satumba na shekarar 1969 a birnin Mashhad da ke arewa maso gabashin Iran, kuma shi ne ɗa na biyu cikin yaya shida na marigayi jagoran ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei.
