Majalisar Dattijan Najeriya ta tabbatar da naɗin Dakta Muttaqha Rabe Darma a matsayin ministan gidaje.
Hakan ya biyo wasiƙar da shugaba Bola Tinubu ya aike wa Majalisar a Jiya, yana buƙatar ta amince da naɗin.
A yayin zaman majalisar, wadda Shugaban majalisar Godswill Akpabio ya jagoranta, ƴan majalisar sun yi wa Dr Darma tambayoyi da dama kan dabarun da zai yi amfani da su wajen magance matsalar ƙarancin gidaje da ƙasar ke fama da ita.
Bayan gamsuwa da amsoshin sa, Majalisar ta amince da naɗa shi.
A ranar 21 ga watan Afrilun 2026 ne Shugaba Tinubu ya yi wasu sauye-sauye a majalisar ministocin ƙasar, inda ya cire tsohon ministan gidaje, Ahmed Musa Dangiwa da na kuɗi, Wale Edun.
